Page Nav

HIDE

Grid

GRID_STYLE

A Cewar Aisha Tsamiya Ba Gobe Ne Daurin Aure Na Ba Sai Nan Gaba Kadan

  A Cewar Aisha Tsamiya Ba Gobe Ne Daurin Aure Na Ba Sai Nan Gaba Kadan BAYA ta haihu. Fitacciyar jaruma A’isha Aliyu (Tsamiya) ta bayyana c...

 

A Cewar Aisha Tsamiya Ba Gobe Ne Daurin Aure Na Ba Sai Nan Gaba Kadan

BAYA ta haihu. Fitacciyar jaruma A’isha Aliyu (Tsamiya) ta bayyana cewa ba a gobe Juma’a, 25 ga Fabrairu, 2022 ba ne za a É—aura mata aure kamar yadda aka yaÉ—a a soshiyal midiya.

Wannan sabuwar sanarwar ta biyo bayan yaÉ—a wani katin gayyatar aure ne wanda aka yaÉ—a a soshiyal midiya, ana cewa na auren jarumar ne.

A katin, an nuna cewa fitacciyar jarumar za ta yi aure a ranar Juma’a, 25 ga Fabrairu, 2022.

A katin, wanda mujallar Fim ta gani, an bayyana sunan sahibin nata, wato Alhaji Buba Abubakar, kuma aka ce za a É—aura auren da misalin Æ™arfe 1:00 na rana a masallacin Sheikh Zarban da ke Kwanar ‘Yanwanki, kusa da gidan Tanko Yakasai da ke unguwar ‘Yankaba, a Kano.

Tun da labarin auren ya É“ulla a soshiyal midiya abokan sana’ar A’isha su ka shiga yi mata fatan alheri, inda kusan dukkan su sun É—ora hoton ta tare da katin auren.

To amma É—azu É—azun ban Aisha Tsamiya ta hau Instagram ta rubuta cewa, “Assalamu alaikum, jama’a barkan mu da warhaka. Na gode da addu’o’in ku da fatan alkhairi, na ji daÉ—i sosai, amma aure na ba 25th ga wannan watan ba ne, sai next month in-sha Allah……Na gode Allah ya saka da alkhairi.”

No comments