Hadiza Gabon Ta Gurfana A Gaban Kotu Hadiza Gabon ta musanta batun auren Bala Musa ne bayan da ta gurfana gaban babbar kotun shari...
Hadiza Gabon Ta Gurfana A Gaban Kotu
Hadiza Gabon ta musanta batun auren Bala Musa ne bayan da ta gurfana gaban babbar kotun shari'a dake Magajin Gari a jihar Kaduna, inda Hadiza Gabon ce bata taba yi masa alkawarin aure ba, hasali ma bata san shi ba kuma bata da wata alaka da shi ta kusa ko ta nesa.Tun da fari dai mutumin mai suna Bala Musa ne ya gurfanar da Hadiza Gabon a gaban Kotun, inda ya bukaci a kwato masa hakkin sa, bayan da ya ce ta ki auren sa duk da alkawarin da suka yi, bayan kuma ta cinye kudin sa har naira dubu 396.
Lauyan Hadiza Gabon Yayi Bayani
Hadiza Gabon ta bakin lauyan ta Mubarak Sani Jibril ta ce tsakanin ta da mutumin bai wuce magoyin bayan ta da suka hadu a shafin ta na Facebook ba, amma babu batun soyayya ko alkawarin aure a tsakanin Su. Legit.ng ta rawaito A bangaren, lauyan wanda ya shigar da kara, Barista N. Murtala, ya ce wanda yake karewa ya hadu da Hadiza Gabon a Facebook, daga nan suka zama abokai. Ya kara da cewa ta yi alkawarin zata aure shi shiyasa yafara kashe mata kudi ba
tare da jin komai ba. "A facebook suka hadu, daga nan suka zama abokai kuma buduwar ta yi alkawarin zata aure shi, shi kuma ya fara kashe mata kudi, amma mun fada wa Kotu zamu gabatar dashaidu kan haka inii lauvan
Hadiza Gabon A Cikin Kotu
Wannan shara'a tafara daukar hankali duba da wasu abubuwa da zamu iya fuskan ta. daga kowanne bangare na wadda ake zargi da wanda yai korafi domin kuwa daga maganar lauyan Hadiza gabon akwai baki biyu walaalla ko a wajen rubuta labarin aka
samu akasi ko kuma tabbas an samu cin karo ko mu da ba masu yanke hukunci ba zamu fahimci akwai tuka da warwara a wannan lafazi Mafi akasari dai kafin wannan zaman kotun ana ganin kamar ba abune mai yiwuwa ace kamar
Hadiza Gabon zata ci kudin mutum da basu taka kara ya karya ba har su dangana da hukuma wanda har kawo yanzu ana tantamar yiwuwar wannan abu wanda wasu ma na zaton masu sojan gona ya hadu
da su ba da ita Suke magana ba amma sai aka jinlauvan ta ya ce sun hadu a Facebook.
Hadiza Gabon Na Fuskantar Barazama
Haka zalika shi kuma ya ta bakin lauyan sa ya tabbatar da zai gabatar da shaidun sa wanda zata iya yiwuwa shaidun su hada da hirar su da suka yi ta sirri ko sakon tafi da gidan ka ko shaidar tura kudi ta hanki da sauran su
Mafi akasari dai kafin wannan zaman kotun ana ganin kamar ba abune mai yiwuwa ace kamar
Hadiza Gabon zata ci kudin mutum da basu taka kara ya karya ba har su dangana da hukuma wanda har kawo yanzu ana tantamar yiwuwar wannan abu wanda wasu ma na zaton masu sojan gona ya hadu
da su ba da ita Suke magana ba amma sai aka jinlauvan ta ya ce sun hadu a Facebook.
Hadiza Gabon Zata Koma Kutu
HADIZA GABON
No comments